Mataimakin
Shugaban Amurka Dick Cheney ya bayyana cewa matukar ana so a
tabbatar da samun zaman lafiya tsakanin Isra’ila da Falasdinawa
to akwai bukatar dukkannin bangarorin su kai zuciya nesa.
Mr Dick
Cheney ya ce batun ware yankin Falasdinawa ya zama mai cin
gashin kansa to fa abu ne da ya dace.
Mataimakin
Shugaban Amurka ya ambata haka ne jim kadan bayan wata
tattaunawar su da shugaban Falasdinawa Mahmud Abbas a Ramallah
da ke yankin gabar kogin Jordan, a wani bangare ziyarar sa
yankin gabas ta tsakiya.