Rahotannin
dake fitowa daga manyan jamian lafiya na kasar Iraki na nuni da
cewa , ana samun karuwar mutanen da suka rasa rayukan su
sakamakon wani hari da aka kai Birnin Karbala a ranar Litinin
din da ta gabata, inda a yanzu hakayawan wadanda suka rasa
rayukan nasu ya kai hamsin.
Shi dai
wannan bam ya tarwatse ne a daf da wani wurin ibada na Imam
Hussain , wand jika ne ga Annabin Tsira MUHAMMD (S.A.W.) kuma
wurin ya kasance wata cibiya ce da mabiya darikar shi a ke yawan
kai ziyara.