Wata yar
kunar bakin wake dake kasar Iraki ta tarwatsa bam da ya kashe
wasu mutane kusan 32 kana wasu 50 suka yi raunuka a birnin
Karballa wuri mafi mahimmanci ga mabiya Shia.
Rahotanni
sun bayyana cewa harin ya aukune kusa da hubbaren Sayyidina
Husseini,Allah ya kara masa yarda
Kazalika
jamian kula da lafiya sun bayyana cewa galibin wadanda hatsarin
ya rutsa da su yan kasar Farisa ko kuma Iran ne..