Bincika
 

Shafi

Barka da zuwa Muryar Nijeriya ............................ Sashen Hausa

Turo E-Mail

Tel: 234- 01- 8799428

Shugaban Sabiya Mr Boris Tadic ya rusa majalisar dokokin kasar tare da ware ranar 11 ga watan mayu domin gudanar da zabe.

Matakin ya biyo bayan durkushewar da gwamnatin Hadaka karkashin jagornci na Firayminsta Vojislav Kostunica ta yi a makon da ya gabata.

Ministocin Sabiya sun kasa cimma daidaito kan jingine huldar zumunci da Kungiyar tarayyar kasashen Turai wato .E.U. domin nuna korofi ga amincewa da yancin Kosovo da wasu mambobin kungiyar ta E.U. suka yi. 

Rundunar sojojin Pakistan ta yi tirr da dakarun kawance karkashin jagoranci na kasar Amurka sabili da harba makami mai kunsau na atilare a iyakar Pakisatan da ya kashe mata biyu da wasu kananan yara guda biyu.

Mai Magana da yawun rundunar sojojin Manjo-Janar Athar Abbas ya ce dakarun kawance wadanda ke fafatawa da yan gwagwarmaya, sun jefa makami mai kunsau daban-daban guda biyar da suka afkawa lardin Waziristan dake yankin arewaci.

Dakarun Amurka sun ce harin wani martini ne ga wata barazanar da aka hakikance.

Sojojin Amurka da na Pakistan suna gwabza fada da mayakan sunkuru na Taliban a iyaka dake tsakanin kasashen Afghanistan da Pakistan.

 

Home | Contact | VON | Contact Us | archive
Webmaster@voiceofnigeria.org :Change Password :VON Staff Sign Up
Copyright© 2007. All Rights Reserved Voice Of Nigeria. Developed by: VON ON-LINE

7255KHz 41m; 9690KHz 31m; 11770KHz 25m; 15120KHz  19m