Shugabannin jamiyyun siyasa guda biyu da suka yi nasara a
zabubbukan kasar Fakistan sun rattaba hannu akan yarjeniyoyin
kafa gwamnatin hadaka a kasar.
Mijin tsohuwar firaminista marigayyiya Benazir Bhutto wato,Asif
Ali Zardari da kuma tsohon Firayminista Nawaz Sherif sun bukaci
shugaba Pervez Musharraf da ya gaggauta kafa majalisar dokokin
kasar.
Jamiyyar dake goyon bayan shugaba Pervez Musharraf ta sha kaye
Zabubbukan majalisar dokokin da aka gudanar a kasar a watan
Fabrairun da ya wuce.
Mr Musharraf ya bukaci gwamnati mai jiran gado da ta mance da
batun siyasa kana ta yi jagoranci na gari.
Yarjeniyoyin game da gwamnatin hadaka za su shafi jamiyyar da
marigayyiya Benezir Bhutto ke jagoranta kafin ta rasu wato
Pakistan Peoples Party da kuma jamiyyar Pakistan Muslim Party ta
Nawaz Sherif.