LABARUN GIDA NIJERIYA
Shugaba
Umaru Musa Yar Aduwa ya taya jiga-jigan shugabanin adawa guda
biyu na kasar, wato Janar Muhahammadu Buhari da kuma tsohon
mataimakin shugaban kasar
Alhaji
Atiku Abubakar, bisa yadda suka yi azamar ci gaban tafarkin
damakuradiya a kasar ta hanyar shigar da karar zaben da bai yi
musu dadi ba.
Shugaba
Yar Aduwa ya nuna farin cikinsa ga jama’a, kan yadda suka mika
masa ragamar shugabanci. Shugaban ya nuna farin cikinsa ne
sa’ilin da yake tarbar .wata babbar tawaga ta shugabannin
jam’iyyarsu ta PDP, da gwamnonin jihohi da ministoci da kuma
sauran masu taya shi murna a fadarsa ta Aso Rock dake Abuja.
Asusun
bayar lamuni na duniya wato IMF ya yi kira ga kasashen Afrika da
su yi koyi da Nijeriya wajen inganta harkokinsu na tattalin
kudaden shiga.
Shugaban
asusun farfesa Dominik Skosan shi ne ya bayyana hakan a wani
taron bita a Abuja babban birnin Nijeriya. Ya kara da cewa
ka’idojin sarrafa kudaden da Nijeriya ke samu daga gurbataccen
man fetur sun taimaka mata wajen gudanar da tattalin arzikin
kasar.
Gwamnan
babban bankin Najeriya Farfesa Chukuma Soludo ya nuna damuwarsa
bisa kokarin sauya fasalin tattalin arzikin kasar da aka kudura
nan da shekara ta 2020, abin da ya ce rashin cikakken tsaro ka
iya janyo masa cikas.
Soludo
yayi wannan maganar ne a Abuja babban birnin Najeriya a yayin da
yake gabatar ababan hawa na tsaro ga rundunar yan sandan
Najeriya.