Shugaban
Najerya Alhaji Umar Musa Yar adua, ya amince da murabus din da
ministan kula da harkokin lafiya ta kasar farfesa Adenike Grange
tayi gami da Ministan kasa a maaikatar Mr. Gabriel Adaku.
Ministocin
biyu dai zasu bar Majalisar zartarwar ta tarayya ne biyo bayan
zargin cin hanci da hukumar kula da masu yiwa tattalin arzikin
Najeriya ta annati wato EFCC ta yi musu.
Kwamitin
kula da harkokin asusun hukumomi da maaikatun gwamnati a
majalisar wakilai ta Najeriya, yayi yunkurin gano wurin da aka
ajiye kudi kimanin Dalar Amurka Miliyan arba in, mallakar asusun
bunkasa fasahar manfetur.
Wannan
kudi dai shi ne abinda hukumar ta samu a matsayin rara wajen
gasar samun rijiyoyin hako mai a shekarun 2004,2005 da kuma
2006, wanda kuma ba a sanya suba cikin a cikin asusun hukumar,
lamarin da ya sabawa dokar data kafa hukumar.
Tashar
Jiragen ruwa ta Houston dake a jihar Texas a kasar A kasr Amurka
na son kulla kawance da takwararta ta Najeriya da nufin bunkasa
cinikayya tsakanin kasa da kasa.