An baiwa
dukkan kamfanonin dake karkashin wani bincike da ake yi kan hada
hadar kudade na shekarar ta 2005 a bangaren man fetir na
Najeriya, makwanni biyu dasu bada cikakken hadin kansu wajan
samar da bincike mai zaman kansa.
A
tattaunawar da tayi da kamfanonin da abin ya shafa a birnin
Abuja hedikwatar Najeriya ,shugabar hukumar tantance yadda
kamfanonin kasar ke gudanar da ayyukansu(NEITI) Farfesa Assisio
Asoubio, ta ce an dauki wannan mataki ne da nufin tabbatar da
cewa an gudanar da binciken yadda ya kamata.
Jamian
hukumar bunkasa yankin Naija-Dalta sun kara jaddada bukatar dake
akwai ta ganin an tabbatar da bin ka’idojin da suka dace wajen
bayar da kwangilar sake gina yankin.
Kwamishinan hukumar mai kula da jihar Ondo kudu maso yammacin
Najeriya Ibukun Omotohinshe,shine ya bayyana haka a babban
birnin jihar dake Akure.Yace daukar wannan mataki ya biyo bayan
munanan matakan da aka shimfida a baya game da bayar da
kwangila kana daga bisani a yi watsi da ita.