Bincika
 

Shafi

Barka da zuwa Muryar Nijeriya ............................ Sashen Hausa

Turo E-Mail

Tel: 234- 01- 8799428

 

Shugaban Nijeriya Alhaji Umaru Musa Yar’adua ya bukaci al’umomin kasar da su yi anfani da ranakun bukukuwan idil maulud da kuma Ista a matsayin wata damar yin tunani mai zurfi game da koyarwa da kuma akidun addinin Islama da kuma na kirista. 

Bayanin hakan na kunshe a sakonsa ga al’umar Nijeriya na barka da idil maulud da kuma ista na wannan shekarar. 

Shugaban yace galibin yan’ kasar na bin daya daga cikin addinan biyu mafi girma a kasar. 

Mataimakin Shugaban Nijeriya ,Dr Goodluck Jonathan ya bukaci al’umomin kasar da su dukufa domin bautawa Allah da kuma yi wa kasa hidima. 

A sakonsa ga mabiya addinin kirista a Nijeriya,Mataimakin shugaban yace su kekashe kasa don ganin ana gudanar da duk wani abu akan kai’da. 

Gwamnatin Jihar Bauchi Arewa maso gabashin Nijeriya ta kebe fiye da Naira Miliyan dubu biyu da rabi domin samar da ruwa mai tsabta ga al’umar jihar cikin watanni 10 da suka gabata.

Kwamishinan kula da albarkatun ruwa na jihar,Alhaji Tanko Dutse ne ya bayyana haka a garin Bauchi babban birnin jihar.

 

Home | Contact | VON | Contact Us | archive
Webmaster@voiceofnigeria.org :Change Password :VON Staff Sign Up
Copyright© 2007. All Rights Reserved Voice Of Nigeria. Developed by: VON ON-LINE

7255KHz 41m; 9690KHz 31m; 11770KHz 25m; 15120KHz  19m