Mai Magana da yawun maaikatar
harkokin wajen nijeriya ya bayyana cewar jagorancin kasar a
kwamiti na musamman kan wanzar da zaman lafiya na majalisar
dinkin duniya baya fuskantar barazana.
A yayin da yake maida martini a
dangane da batun sahihancin jagorancin kasar a kwamitin ayyukan
zaman lafiya na majalisar dinkin duniya a Abuja fadar gwamnatin
nijeriya, Mr. Olukanni yace dan tsaikon da aka samu na tura
babban jakadan kasar zuwa majalisar dinkin duniya bai kawo wani
babban gibi ba gami da shafar kasar wacce ta shafe shekaru goma
tana shugabancin kwamitin tabbatar da zaman lafiya na majalisar
dinkin duniyar.
Kazalika Mr. Olukanni yace wannan
karramawar da aka yiwa kasar ya biyo bayane a dangane da irin
rawar da kasar take takawa tun shekarar 1960 a matsayin wata
kasa dake da dakarun wanzar da zaman lafiya masu yawa na
majalisar dinkin duniya, haka kuma Mr. Olukanni ya kara da cewar
a yanzu haka nijeriya tana da jakadu a wasu manyan kasashe kamar
su Jamus, Beljium, Habasha. Israila, Indiya, Swiziland gami da
ofishin majalisar dinkin duniya dake a Geneva.
Aranar laraban nan ne musulmi a
duk fadin duniya suka gudanar da bikin tunawa da ranar haihuwar
fiyayyen halitta annabi Muhammmad tsira da amincin allah su
tabbata a gareshi.
Wannan ranar dai musulmai na
amfani da ita ne domin gudanar da karatun Alqurani mai girma
gami da yin nazarin kyawawan dabiun fiyayyen halitta annanabi
mohammad tare da karanta litattafan addini a duk daukacin daren
ranar goma sha biyu ga watan Rabiul awwal, wanda ya kasance wata
na uku dake a cikin kalandar addinin musulunci.
An kalubalanci maaikatan jarida
da su kawar da munanan manufofin da ake alakantawa ga addinin
Islama.
Shugaban kungiyar kafafen yada
labaru ta Najeriya (BON) Alhaji Abubakar Jijiwa shi ne yayi
wannan kiran a Abuja babbab birnin tarayyah a yayin taron tunawa
da fiyayyen halitta Annabi Muhammad (S.W.A.) da kungiyar
musulmai yan jaridu nijeriya ta shirya a abujan.
A cikin wadanda suka sami dammar
halartar taron ciki hadda babban jakadan kasar parisa a nijeriya
sai mr,isah cosuro kesasaga gami da wasu futattun yan jaridu
dake a nijeriya.