Ministan
kula da aikin gona da albarkatun ruwa a Nijeriya Dakta Abba
Sayyadi Ruma ,ranar talatar nan 18 ga watan Maris shekara ta
2008 ya yi bayani ga taron manema labaru game da ranar ruwa ta
duniya da kuma kaddamar da ranar tsabtace muhalli ta kasa da
kasa.
Wakilin
Asusun kula da harkokin yara na Majalisar dinkin duniya wato
UNICEF Mr Ayalew Abai da wasu shugabanin hukumomin Majalisar
dinkin duniya dake Nijeriya da Kungiyoyi masu zaman kansu da
kuma masu ruwa da tsaki ne suka halarci taron.
Kotun
sauraron kararrakin zabe a Nijeriya ta amince da zaben gwamnan
jihar Oyo kudu maso yammacin Nijeriya Cif Adebayo Alao-Akala.
Duk da
cewa Alkalai uku na kotun sun amince da zaben,daya daga cikinsu
ya bukaci a soke zaben sabili da an hana wasu yancin kada kuria.
Dan
takarar neman mukamin gwamna karkashin jamiyyar A.N.P.P. M r
Abiola Ajumobi ne ya hade da wasu jamiyyu biyar na yan adawa
domin kalubalantar zaben Cif Adebayo Alao-Akala wanda aka zaba
watan Afrilun shekarar 2007.
Masu karar
sun yi ikirarin cewa kwamitin binciken da tsohon gwamnan jihar
Oyo Alhaji Rashid Ladoja ya kafa ya samu gwamna Aalao-Akala da
laifin aikata ba daidai ba..
Yan adawar
suna masu tambaya game da yadda gwamnan ya bar aikin dansanda
wanda aka yi masa ritayar dole domin ladabtarwa sakamakon laifin
da ya aikata..
Shugaban
kwamitin kula da harkokin muhalli na majalisar dokokin jihar
Lagos kudu maso yammacin Nijeriya Mr Adesina Ogunkoya, ya
bayyana cewa gwamnati ta ware Naira miliyan 500 domin inganta
magudanun ruwa na jihar.
Mr Adesina
Ogunkoya ya fada a birnin Lagos cewa zaa yi amfani da kudin
domin samar da magudanun ruwa da kuma yashe mashigan ruwa a
tsawon kilomita 52.
Shugaban
kwamitin kula da muhalli ya ce hukumomi a jihar sun shirya
Tsab domin
yin amfani da kudin wajen ginawa da kuma yashe magudanun da kuma
wasu mashigan ruwa,da nufin maganta matsalar ambaliyar ruwa.a
Birnin Lagos da kewaye.