Ranar Litinin 10 ga watan Maris wakilai na Tarayyar Turai E.U. da
abokan hadin gwiwa guda 2 na Majalisar dinkin duniya za su yi
taro da kuma tatance ci gaba da Nijeriya ta samu game da samar
da ruwa mai tsabta da kuma kula da muhalli a kasar.
Bayanin haka na kunshe a wata takardar sanarwa da asusun kula da
harkokin yara na majalisrdinkin duniya wato UNICEF ya gabatar a
babban birnin Nijeriya.
Takardar sanarwar na dauke da sa hannun masanin harkokin
sadarwa,kafafan yada labarai da hulda da kasashen ketare na
UMICEF dake Nijeriya, Mr Geoffrey Njoku.
Gwamnatin Nijeriya ta aike sakon taaziyya ga al-ummar jihar
Katsina dake arewacin Nijeriya sabili da rasuwar Mai Martaba
Sarkin Katsina Alhaji Muhammad Kabir Usman.
A maraicen asabar nan ne aka yi jana izar marigayin a Katsina
wanda ya rasu a safiyar ta asabar a babban asibitin kasa dake
Abuja hedkwatar Nijeriya.
Mataimakin shugaban Nijeriya Dr Goodluck Jonathan wanda
sakataren gwamnatin kasar Alhaji Babagana Kingibe da wasu
kusoshin gwamnatin kasar suka rufa masa baya ne ya jagoranci tawagar
zuwa fadar Sarkin domin yin gaisuwar taaziyya.
Gwamnan jihar Katsina Alhaji Ibrahim Shehu Shema da kuma wasu
manyan baki ne suka tarbi ayarin na gwamnatin Nijeriya.