Darakta
janaral kuma mataimakin sakataren hada hadar ciniki da kasuwanci
na kasar Amurka Isra’il Hernendez zai jagoranci wata tawaga zuwa
wasu kasashen nahiyar afrika,ciki har da Nijeriya da nufin kulla
yarjejeniyar huldar kasuwanci a kasashen.
Har ila
yau tawagar ta hada da jami’an kanfanoni 13 na kasar Amurka
wadanda zasu zu neman abokan huldar cinikayya a Nijeriya.
Mr
Hernaendaz ya bayyana fatansa na jawo wasu manya kuma ingantattu
kanfanonin a kokarinsa na kulla huldar cinikayya ga kasar
Ghana,Nijeriya,da kuma Afrika ta kudu.
Gwamnatin
Nijeriya za ta daukaka darajar wasu filayen tashi da saukar
jiragen sama na kasa da kasa da nufin gudanar da hada hadar su
cikin sauki.
Ministan
kasa a ma’aikatar jiragen sama Felix Hassan Hyet shi ne ya
bayyana haka ga manema labaru a bayan wata tattaunawa da
shugaban Nijeriya Alhaji Umaru Musa Yar’adua ya yi da masu ruwa
da tsaki a harkokin hada hadar jiragen sama da ya gudana a Abuja
hedikwatar kasar.
Filayan
tashi da saukar jiragen saman kasa da kasa da za a daukaka
darajar su sun hada da na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja babbam
birnin Kasar,sai na Mallam Aminu kano a jihar Kano arewa maso
yammacin Nijeriya,kana da na jihar Legas kudu maso yammacin
kasar,a karshe da na Fatakwal da ke kudancin kasar.