Gwmnatin
Najeriya ta yunkura domin sake yin nazari game da dokokin yawon
bude ido
da kuma al adu na kasar.
Ministan
yawon bude ido ,aladun gargajiya da wayar da kan jamaa a Najeriya,Yerima
Adetokunbo Kayode shine ya bayyana hakan a Abuja babban birnin
Najeriya.
Ministan
ya ambata wadanan kalaman ne yayin da yake yiwa manema labari
bayani game da alkibilar da maakatarsa ta sanya gaba a shekara
ta 2008.
Yerima
Kayode y ace hukumomi a Najeriya za su rinka sabunta kaidodi dakuma
dokokin da suka shafi fanonin yawon bude ido,aladun gargajiya
domin su dace wannan zamani.
Hukumar
kula da ingancin magunguna da abinci ta kasa a Najeriya wato NAFDAC,
ta dukufa domin ganin ana buga gargadi ballo-ballo a fakitin sigari
ga masu zukar taba.
Darakta
janar ta hukumar, Farfesa Dora Akunyili,,it ace ta bayyana hakan
a hedkwatar kasar Abuja yayin wan taro na kasa game da matasa.
Farfesa
Dora Akunyili ta bayyana takaici game da wasu da suka rungumi
akidar shan taba a tsakanin jamaa..
Ta
ce hukumar NAFDAC za ta aike sakonni ga kamfanonin sigari don
su buga sakonnin gargadi dalla-dalla a fakitin sigari.