Search Engine
 
 

Shafi.......................... Nijeriya ............... Afrika............... labaran duniya

Barka da zuwa Muryar Nijeriya ............................ Sashen Hausa

Turo E-Mail

Tel: 234- 01- 8799428

 

Hukumar kula da harkokin makamashin Niukiliya a Nijeriya ta fara bayar da horo ga Jamianta domin tabbatar da kariya wajen yin amfani da cibiyoyi da kayayyakin makamashi a  Kasar.

Wannan horon dai na gudana ne tare da hadin gwiwar Hukumar kula da makamashin Niukiliya ta Duniya,mai mazauni a Birnin Vienna na kasar Austria.

A lokacin bukin bude taron bayar da horon,Shugaban hukumar a Nijeriya,Farfesa Shamsuddeen Elagba,yayi nuni da cewar horon zai bunkasa yin amfani da makamashin Niukiliya domin samar da wutar lantarki.

A nashi jawabin,wakilin hukumar kula da makamashin Niukiliya ta kasa da kasa,Dakta Rustin  Passi,wanda kuma daya ne daga cikin masu bayar da horon ,ya bayyana cewar hukumar kula da makamashin  Niukilya ta kasa da kasa zata taka rawar kayyade bada lasisi da sanya – ido da kuma kayyade daukacin aikin hukumar. 

Ofishin  Jakadancin Nijweriya  dake kasasr Birtaniya ya karrama wasu yan Nijeriya guda biyu saboda ficen da suka yi a kasar.

Wadanda Ofishin ya karrama dai,sune  Ibrahim Baba Shehu da Chinwe Chiduben dake karan jamia a kasar ta Birtaniya sakamakon rawar ganin da suka taka a jamioin da suke karatu.


 
 
 

Home | Contact | VON | Contact Us | archive
Webmaster@voiceofnigeria.org :Change Password :VON Staff Sign Up
Copyright© 2007. All Rights Reserved Voice Of Nigeria. Developed by: VON ON-LINE

7255KHz 41m; 9690KHz 31m; 11770KHz 25m; 15120KHz  19m