LABARUN DUNIYA
Shugaban
adawar kasar Kenya Raila Odinga yayi kira ga magoya bayansa da
su janye zanga-zangar da aka shirya yi don hura wa gwamnati wuta
akan shirin raba madafan iko domin kawo karshen rikice-rikicen
zaben siyasar kasar.
Mr Odinga
ya shaidawa manema labarai cewar jam’iyarsu ta ODM ta gamsu da
ganawar da suka yi da tsohon maga-takardar majalisar dinki
duniya Kofi Annan. A saboda haka ne suka janye zanga-zangar da
suka yi niyyar yi har zuwa wani lokaci.
A Khartun
kuma babban birnin Sudan dubun dubatar mutane ne suka yi
zanga-zangar nuna bacin rai game cin zarafin da aka yi wa
addinin Musulunci ta hanyar buga wani hoto da suke cewa ma’aiki
ne.
An sake
buga hoton cin zarafin ne bayan shekaru biyu da suka wuce wato a
shekara ta 2006. Wanda hakan ya haddasa zanga-zanga a duniya
baki daya.