Shugaban
kasar Zumbabuwe Robert Mugabe ya zargi jam’iyun adawar kasar da
yunkurin kulla makarkashiya da tsohuwar kasar da ta yiwa
Zumbabuwe mulkin mallaka wato Burtaniya,domin kifar da
gwamnatinsa.
Shugaban
dan shekaru 84 a duniya da yake fatan ganin an sake zabar sa a
matsayin shugaban kasa waadin shekaru 5 masu zuwa.
Kazalika a
wuri guda yana fuskantar kalubale daga tsohon ministan kudi a
gwamnatinsa Mr Simba Makoni kana da jagoran jam’iyar Movement
for Democratic Change MDC Morgan Chingarai.