Kasar
Birtaniya ta kare kanta dangane da mataki da ta dauka na maida
‘yan kasar Zimbabwe masu neman mafaka zuwa ga kasarsu ta
haihuwa.
Kimanin
‘yan kasar dari biyar ne suka karbi takardunsu na neman su
gaggauta komawa gida ko kuma su fuskanci tilastawa daga
bangaren hukumomin Burtaniya.
Cikin
wadannan mutane wani ya bayyana cewa abin mamaki ne ga Birtaniya
ta yi watsi da cin zarafin alummar kasar da akayi a baya kana
ta yi kokarin tilastawa mutane komawa gida.
Sarah
Harland ta gano cewa kiran babban zaben kasar wanda aka shirya
yinsa anan gaba,abune wanda aciki ake saran aikata adalci.
Har ila
yau Uwargida Sarah mamba cikin wata kungiya dake kasar wacce ke
taimakawa wadanda suka rasa mafakar ta bayyana cewa akwai
bukatar canji ainda ta kara da cewa maida wadannan mutane kasar
a halin yanzu abune wanda bai dace ba.
Kungiyar
fafutikar hakkin bil Adama dake birnin New York na kasar Amurka
ta bayyana cewa rikicin kabilanci daya biyo bayan Zaben shugaban
kasar Kenya a watan Disambar bara abune da aka kirkiro shi .
Kungiyar
ta ce kai farmaki kan alummar kikuyu ta shugaba Mwai kibaki abu
ne da sarakuna suka kulla makarkashiya a matsayin maida martini
kan abokan adawaarsu .
Wannan
kungiya ta bukaci da a gaggauta gabatar da wadannan shugabanni
a gaban kuliya manta sabo bisa laifin sanya hannaye wajan tayar
da tarzoma wacce tayi sanadiyyar kisan sama da mutane dubu daya
da kuma sanya wasu jamaa sama da dubu dari shida su kauracewa
gidajensu.
Kazalika
rahotanni sun dora alhakin ga jamian ‘yansanda wadanda suka yi
amfani da karfi fiye da kima kan ‘yandawa saadda suke zanga
zanga .
Tuni dai
dan adawa Raila Odinga ya sa hannu kan yarjejeniyar raba madafun
iko da shugaba Mwai Kibaki wanda kuma kungiyar tayi murna da
yin hakan.