Gwamnatin
Cadi ta ce dakarun yan tawaye dauke da miyagun makamai sun shige
mata kasa ta gabashi daga Sudan.
Wata
sanarwa ta Gidan rediyon kasar ta ce sojojin hayar sun tsallaka
iyakarta ne a yankin Moundeina,arewa da iyakar garin Ade.
Idan ba a
manta ba a watan jiya yan tawaye sun yi wani kokarin da ya ci
tura na kifar da gwamnatin Shugaba Idris Derby.
Yanzu haka
Shugaba Idris Derby da Shugaba Omar al-Bashir na Sudan sun sa
hannu akan wata yarjejeniyar hana goyon bayan yan tawayen wajen
kai hari cikin kasashen juna.
Sakatare
janar na majalisar dinkin duniya Mr Ban Ki-Moon shi ne ya
shugabanci sa hannu kan yarjejrniyar a Dakar babban birnin kasar
Sinigal.
Gwamnatin
Sudan ta yi fatali da sukar da Amurka ta yi cewa Sudan na take
hakin bil Adam.
Sudan ta
ce gwamnatin shugaba George Bush ce tafi kowace kasa game da
take hakkokin dan Adam kuma mai bakin ciki da duk wasu ayyukan
ci gaba da hukumomi a birnin Khartoum suka samu.
Wata
majiyar Amurka ta bayyana cewa ana ci gaba da kashewa da kuma
azabtar da mutanen da ba su ji ba, ba su gain ba da kuma yiwa
mata fyade.