Hausa Archive

 
Search Engine
 
 

Shafi.......................... Nijeriya ............... Afrika............... labaran duniya

Barka da zuwa Muryar Nijeriya ............................ Sashen Hausa

Turo E-Mail

 

Mahaukaciyar guguwar nan wato JOKWE ta lalata kusan gidaje 500 da kuma kashe mutun guda a yankin arewacin kasar Muzambik, a ranar lahadin nan.

Shugaban sashen kula da yanayi na kasar,Musa Mustafa, ya ce guguwar ta yi mummunar ta adi a tsibirin Madagasca.Musa Mustafa ya ce mai yiwuwa guguwar Jokwe ta kara yin wata barna a litinin nan. 

Hukumar kula da shaanin dokoki a kasar Afrika ta kudu ta gabatar da sabon tsarin da zai lalubo dokokin da suke da alaka da nuna wariya a kasar.

Tsarin zai yi gyare-gyare akan dokoki 2,800 wadanda aka kafa a kasar tun daga shekarar 1910.

Wata Alkali a kotun tsarin mulkin kasar Afrika ta Kudu,Yvone Mokgoro ta ce babban dalilin gabatar da wannan sabon tsari shine maida samar da dokokin da za su dace da zamani.

Kazalika wasu kwararrun ahrkokin dokoki za su bada tasu gudumowar domin gabatar da tsarin mulkin da ya soke dukkan sassa masu alaka da nuna wariyar launin fata a kasar.

 

 
 
 

Home | Contact | VON | Contact Us | archive
Webmaster@voiceofnigeria.org :Change Password :VON Staff Sign Up
Copyright© 2007. All Rights Reserved Voice Of Nigeria. Developed by: VON ON-LINE

7255KHz 41m; 9690KHz 31m; 11770KHz 25m; 15120KHz  19m