Shugaban
kasar Kenya `Mwai Kibaki tare da fira minister da ke shirin fara
aiki Raila Odinga na gudanar da zaman ganawa na musamman.
Zaman
ganawar dai ya kasance na farko tun bayan lokacin da suka
rattaba hannu ga shirin samar da gwamnati da zata raba madafun
iko.
Tuni dai
Mr Odinga ya bayar da haske ga mambobin majalisar dokokin na
jam’iyun guda biyu da su gudanar taron fahimtar juna kafin zaman
da majalisar za ta yi a ranar Alhamis.