Search Engine
 
 

Shafi.......................... Nijeriya ............... Afrika............... labaran duniya

Barka da zuwa Muryar Nijeriya ............................ Sashen Hausa

Turo E-Mail

 

Babban magatakardar majalisar dinkin duniya Mr Ban Ki-Moon ya yi kira ga shugabanni a kasashen Sudan da Cadi da su inganta matakan tsaro ,daiadai lokacin da gwamnatin jumhuriyar Cadi ta ce yan tawaye sun kara kusantar birnin Njamena hedkwatar kasar.

Mr Ban Ki-Moon ya yi wannan tsokacin ne a kasar Habasha, yana mai cewar ,tsaurara tsaro na da mahimmanci sabili da yan tawaye sun kutsa kai a yankin gabashin cadi.

Ya bukaci kasashen Cadi da Sudan da su sanya ido sosai game da jamian tsaro dake iyakokinsu.

Kasashen 2 na zargin juna da tallafawa yan tawayaen.


Kungiyar Tarayyar kasashen Afrika wato A.U. ta zabi shugaban kasar Tanzania Mr Jakaya Kikwate a mukamin sabon shugabanta.

Yayin taro karo na 10 wanda shugabannin gwamnatoci da kasashe suka yi a Adia-Ababa babban birnin kasar Habasha ne Kungiyar ta A.U. ta zabi Mr Kikwate.

A jawabinsa ga Tsohon shugaban A.U. Mr John Kuffour na kasar Ghana ya bukaci a maida hankali sosai akan sake maida zaman lafiya da lumana a kasashen Sudan da Somaliya da kuma sauran sassan nahiyar ta Afrika.

 
 
 

Home | Contact | VON | Contact Us | archive
Webmaster@voiceofnigeria.org :Change Password :VON Staff Sign Up
Copyright© 2007. All Rights Reserved Voice Of Nigeria. Developed by: VON ON-LINE

7255KHz 41m; 9690KHz 31m; 11770KHz 25m; 15120KHz  19m