Search Engine
 
 

Shafi.......................... Nijeriya ............... Afrika............... labaran duniya

Barka da zuwa Muryar Nijeriya ............................ Sashen Hausa

Turo E-Mail

Tel: 234- 01- 8799428

 

Bangarorin siyasar dake takun saka  a kasar Kenya,sun sha alwashin hanzarta yin tattaunawa  da nufin warware takaddamar da suka dade suna yi akan arziki da filaye ,sanadiyyar rigingimun da suka biyo bayan zabukan kasar  wanda kuma ya zubar da martabar ta a matsayin daya daga cikin kasashen afrikar dake da  daidaiton shaanin siyasa.

Alummar kasar Kenya dai,bayan tayi fama da matsalolin sace-sace,da kone-kone da kuma kasha-kashen kabilanci,sakamakon takaddamar data biyo bayan Zaben ranar ashirin da bakwai dga wata Disambar bara,a yanzu ta yi marhabin lale da gwamnatin hadin kan kasa,wadda aka cimma yarjejeniyar kafa- ta a makon da ya gabata,domin kawo karshen tashin hankalin da ya fatattaki masu yawon bude-ido a kasar ,kana da janyo koma-baya ga tattalin arzikin kasar.

Yarjejeniyar,wadda tsohon Sakataren  Majalisar dinkin duniya Mr Kofi Annan,wanda kuma shine babban mai shiga tsakani ya jagoranci kulla ta,zata dubi batun filaye da samar da sauye-sauye ga shaanin Zaben kasar.

Mr Annan,wanda ya mika aikin shiga tsakanin ga tsohon ministan kula da harkokin ketare a Nijeriya  Farfesa Oluyemi Adeniji,ya bayyana cewar kamata yayi a warware dukkan batutuwan da aka dade ana jayayya akan su cikin waadin shekara guda,amma yan siyasar da ake tattaunawa dasu sun bayyana cewarsuna fatan hanzarta aikin su.  

 

 

 
 
 

Home | Contact | VON | Contact Us | archive
Webmaster@voiceofnigeria.org :Change Password :VON Staff Sign Up
Copyright© 2007. All Rights Reserved Voice Of Nigeria. Developed by: VON ON-LINE

7255KHz 41m; 9690KHz 31m; 11770KHz 25m; 15120KHz  19m